APC 2027: ANPP na neman a bar mata mataimakin shugaban ƙasa

Zaben APC 2027, Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa jam’iyyar APC mai mulki na iya fuskantar matsaloli iri ɗaya da suka addabi wasu tsofaffin jam’iyyun adawa a Najeriya, musamman dangane da rashin daidaito a cikin gida.
Wannan ra’ayi ya biyo bayan wasu kalamai daga ɓangaren tsohuwar jam’iyyar ANPP — ɗaya daga cikin jam’iyyun da suka haɗu suka kafa APC — inda suka nemi a bai wa ƴaƴansu damar samun kujerar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Wasu daga cikin waɗanda suka fito daga ANPP sun bayyana bukatar ganin an bai wa tsoffin mambobin jam’iyyar guraben jagoranci a cikin gwamnatin APC. A cewarsu, ya kamata a ba su wakilci daidai da irin gudunmuwar da suka bayar tun kafuwar jam’iyyar a shekarar 2013.
A wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja, sun jaddada cewa bai kamata a manta da irin rawar da suka taka ba, tun daga kafa jam’iyyar har zuwa samun nasarar da APC ta samu a zaɓen 2015.
Sun kuma buƙaci hadin kai da adalci daga gwamnatin shugaba Bola Tinubu, tare da jan hankali cewa kamata ya yi a duba bukatunsu cikin hikima da fahimta, domin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan jam’iyyar.