• Latest
  • Trending
  • All
  • News
  • Politics
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

October 29, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

February 23, 2026
PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

February 22, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

February 19, 2026
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

January 9, 2026
AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in  Quarter-Final

AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in Quarter-Final

January 9, 2026
Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

January 9, 2026
Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

January 8, 2026
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
Monday, March 2, 2026
  • Login
NgHausa
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgHausa
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Blog

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

by NgHausa
October 29, 2025
in Blog
0
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
495
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Kabiru Abubakar Aliyu, wanda aka fi sani da Nakwango, ɗaya daga cikin fitattun dattawan masana’antar Kannywood, ya bayyana yadda ya fara harkar wasan kwaikwayo tun a shekarun 1970, kafin daga bisani ya shiga harkar fim a 1994/1995.

A cewarsa, a farkon lokacin yana fitowa ne a matsayin mace, saboda murya tasa tana da laushi wanda ya dace da irin wannan rawa.

Fim ɗinsa na farko shi ne Kilu ta Ja Bau na Hamisu Iyantama, sannan a shekarar 1995 ya fito a fim ɗin So Ne Ko Kauna ƙarƙashin kamfanin Dabo Films — wanda shi ne fim na farko a harshen Hausa da aka nuna a sinima a Kano.

Nakwango ya musanta zargin da ake yi cewa duk ‘yan fim marasa tarbiyya ne, inda ya jaddada cewa “a kowace sana’a akwai nagari da marasa nagarta.”

Ya bayyana cewa ya rage fitowa a fina-finai ne saboda yawancin sabbin fina-finai yanzu ba sa ɗauke da darasin addini ko na al’ada. Ya ce sai dai idan fim ya shafi kira ga Allah ko nuna al’adun Hausawa, to zai shiga.

See also  Tattaunawa da Nusaiba Muhammad Ibrahim (Sailuba)

Fitaccen ɗan wasan ya kuma soki sabon salo na fina-finai, inda ya kira su “fina-finan harshen Hausa” maimakon “fina-finan Hausa na gaske.”

A cewarsa, yawanci suna gauraya Hausa da Turanci, suna kuma ƙunshe da tashin hankali da kwaikwayon rayuwar Turawa — abin da ke lalata ƙimar da tsaftar masana’antar Kannywood.

Duk da haka, Nakwango ya ce bai taɓa nadamar shiga harkar fim ba, domin ta ba shi girmamawa da albarka da ya kejin daɗi a yau.

Ya ƙara da cewa, “na samu taimako a lokuta da dama saboda mutane sun sanni daga cikin fina-finai.”

Ya kuma tuna wani lokaci da aka kama shi bayan ya tsaya wa wani mutum a kotu wanda ya gudu, amma daga bisani aka sake shi saboda shahararsa.

See also  "Ban taɓa soyayya da jarumi a Kannywood ba – sai dai El-Mu’az, Allah ya yi masa rasuwa" — Jaruma Hannatu Bashir

A cewar Nakwango, ɗansa yana daga cikin manyan editocin fim a Najeriya, kuma ya yi imanin cewa matsayin da Allah ya ba shi cikin masana’antar fim alheri ne daga ƙaddara.

A ƙarshe, ya shawarci abokan aikinsa da su ji tsoron Allah, su kare addini da al’adun Hausawa, su kuma riƙa yafe wa juna.

Haka kuma, ya roƙi al’umma da kada su gaggauta yanke hukunci kan masu fim, domin su ma suna da nagarta da niyyar kawo ci gaba.

Share this:

  • Share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Share on X (Opens in new window) X
Share198Tweet124Share50
NgHausa

NgHausa

NgHausa

Copyright © 2017 JNews.

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

Copyright © 2017 JNews.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks