• Latest
  • Trending
  • All
Goodluck Jonathan 2027 – Muhawara kan Halascin Takararsa a Najeriya

Goodluck Jonathan 2027: Muhawara kan kundin tsarin mulkin Najeriya

October 2, 2025
Nnamdi Kanu Ya Amince Zai Tuntubi Lauyoyinsa Kafin Ya Fara Kare Kansa

Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi

November 20, 2025
ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

November 20, 2025
NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

November 17, 2025
Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

November 15, 2025
Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

November 13, 2025
Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

November 12, 2025
Matsalar Tsaro a Kano: 'Yan sa kai na ƙauyen Shanono suna sintiri domin kare al’umma daga harin ƴan bindiga.

Matsalar Tsaro a Kano: ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Faruruwa, Sun Yi Garkuwa da Mata Biyar

November 12, 2025
NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

November 11, 2025
Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

November 11, 2025
Tsohon Gwamnan Rivers Nyesom Wike tare da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Alkali James Omotosho yayin rikicin siyasa na dokar ta-baci a Jihar Rivers, Najeriya, 2025.

Rikicin Siyasar Jihar Rivers: Wike, Tinubu, da Alkali James Omotosho

November 11, 2025
Dharmendra Ya Kwantar da Hankalin Masoyansa Bayan Shiga Asibiti

Dharmendra Ya Kwantar da Hankalin Masoyansa Bayan Shiga Asibiti

November 10, 2025
Farkon Shirin Super Eagles Don Wasan Takarar Karshe Na Fifa World Cup 2026 a Rabat

Farkon Shirin Super Eagles Don Wasan Takarar Karshe Na Fifa World Cup 2026 a Rabat

November 10, 2025
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
Friday, November 21, 2025
NgHausa News
  • Login
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
No Result
View All Result
NgHausa News
No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
🚀 Join Our Telegram Community

Goodluck Jonathan 2027: Muhawara kan kundin tsarin mulkin Najeriya

by NgHausa
October 2, 2025
in Blog
0
Goodluck Jonathan 2027 – Muhawara kan Halascin Takararsa a Najeriya

Goodluck Jonathan

0
SHARES
53
VIEWS

Yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen 2027 a Najeriya, wata sabuwar muhawara ta ɓarke kan halascin tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ya sake tsayawa takara.

A ƙarƙashin dokokin Najeriya, mutum ba ya wuce sau biyu a zaɓe a matsayin shugaban ƙasa. Wannan ya sanya wasu na ganin Jonathan ba shi da hurumin tsayawa takara, domin ya sha rantsuwar kama aiki sau biyu. Sai dai magoya bayansa na cewa abin da kundin tsarin mulkin ya tanada shi ne zaɓe sau biyu, ba wai rantsuwa ba.

Wannan batu ya janyo zazzafar muhawara tsakanin ƴan siyasa da masana shari’a, inda aka rarrabu kan fassarar sashe na 137 (III) na kundin tsarin mulkin da aka yi masa gyara a 2017.

Mulkin da Jonathan ya yi a baya

Goodluck Jonathan ya fara zama shugaban ƙasa a 2010 bayan rasuwar Umaru Musa Ƴar’adua. Ya yi saura wa’adin shekaru biyu da suka rage, kafin ya tsaya takara a 2011, inda ya yi nasara.

See also  Amaryar TikTok Ta Fadi Matsalar da Jaruman Kannywood ke Fuskanta

Bayan haka aka sake rantsar da shi karo na biyu, inda ya yi wa’adin shekara huɗu (2011 zuwa 2015). Jimillar shekarun mulkinsa ya kai shida.

Me doka ta ce?

Barista Abba Hikima Fagge, lauya kuma masanin kundin tsarin mulki, ya ce kundin tsarin mulkin ya fayyace cewa duk wanda ya yi wa’adin mulki biyu ba ya da ikon sake tsayawa takara.

Ya ce idan aka rantsar da mataimakin shugaban ƙasa domin ya ƙarasa wa’adin wanda ya mutu ko aka tsige shi, wannan za a ƙirga shi a matsayin wa’adi guda, koda kuwa bai cika shekara huɗu ba.

Shin Jonathan na da damar sake tsayawa takara?

Barista Hikima ya ce gyaran kundin tsarin mulkin da aka yi a 2017 ba ya waiwaye baya, saboda haka ba ya shafar Jonathan da mulkinsa da ya ƙare tun 2015.

See also  Rarara Builds Three Primary Schools In Katsina State

A cewarsa, idan aka yi amfani da ƙa’idar doka ba ta waiwaye, to tsohon shugaban ƙasar na iya tsayawa takara. Har ma ya ambaci cewa kotu ta taɓa tabbatar da cewa Jonathan na da damar tsayawa takara, duk da cewa daga baya kotun ɗaukaka ƙara ta kori ƙarar bisa dalilan fasaha na shari’a.

Matsayin Kotun Ƙoli

Duk da haka, lauyan ya bayyana cewa kotun ƙoli ce kaɗai za ta iya yanke hukunci na ƙarshe kan wannan muhawara.

“Idan ana son samun cikakken bayani, dole ne a je kotun ƙoli domin ita ce za ta fayyace wannan dambarwa,” in ji shi.

Jonathan bai bayyana aniyarsa ba

Har yanzu dai Goodluck Jonathan bai fito fili ya ce zai tsaya takara a 2027 ba. Sai dai rahotanni daga makusantansa na cewa yana tattaunawa da abokan shawararsa.

See also  Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

Idan ya tsaya takara kuma ya samu damar yin nasara, zai zama mutum na farko a tarihin Najeriya da ya taba rike shugabancin ƙasa sannan ya dawo takara bayan tsawon shekaru da saukarsa daga mulki.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X
Join our WhatsApp Channel
NgHausa

NgHausa

Related Posts

Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

by NgHausa
September 25, 2025
0

Shin akwai buƙatar tantance masu wa'azi a Kano? A ranar Larabar nan ne dandazon wasu mazauna birnin Kano suka gudanar...

Trump Attends the Return of the Remains of the Navy SEAL Who Died in Yemen

by NgHausa
September 6, 2025
0

Dropcap the popularization of the “ideal measure” has led to advice such as “Increase font size for large screens and...

Amaryar TikTok Ta Fadi Matsalar da Jaruman Kannywood ke Fuskanta

Amaryar TikTok Ta Fadi Matsalar da Jaruman Kannywood ke Fuskanta

by NgHausa
May 6, 2025
0

Hafsat Tuge, wadda aka fi sani da Amaryar TikTok, ta ce mutane suna kallon 'yan fim mata da wani kuskuren...

Garba Muhammad: Daga Cikon Benci Zuwa Tauraro a Fim

Garba Muhammad: Daga Cikon Benci Zuwa Tauraro a Fim

by NgHausa
December 24, 2024
0

Fitaccen jarumin nan da ya shahara a duniyar fina-finan Hausa, Garba Muhammad, wanda aka fi sani da Baban Ma'u a...

Recent Posts

  • Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi
  • ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba
  • NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya
  • Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa
  • Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Recent Comments

  1. Yusuf tanko on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  2. Abdulazeez jibrin on Yadda Zaka Samu Tallafin Kudi a Najeriya (2025): Matakai da Sharuɗɗa
  3. Bashir Gamzaki on COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 PROF. Isah Ali Ibrahim Pantami
  4. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  5. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”

Archives

  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024

Categories

  • Blog
  • Entertainment
  • Hausa Series
  • KannyWood
  • Labaran Duniya
  • Lafiya
  • Nigeria
  • Nishadi
  • Opportunity
  • Siyasa
  • Sports
  • TAFSEER
  • Wasanni
NgHausa News

© NG Hausa News – 2025

Navigate Site

  • About Us
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood

© NG Hausa News – 2025

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks