Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa matakin tallafawa Yan bindiga da suka tuba ya samo asali ne daga bukatar magance manyan dalilan da suka jefa su cikin aikata laifi, musamman rashin ilimi da rashin aikin yi.
A cewar gwamnati, waÉannan dalilai ne suka taka muhimmiyar rawa wajen haifar da matsalar tsaro da jihar ke fama da ita.
Kwamishinan tsaro na jihar, Dokta Nasiru Matazu, ya bayyana cewa Yan bindiga da suka tuba suka mika wuya sun roki gwamnati ta samar musu da makarantu domin Ęara ilimantar da yaransu, asibitoci don kula da lafiyarsu, da kuma wuraren shan ruwa ga shanunsu.
Ya ce samar da waÉannan abubuwa zai taimaka wajen tabbatar da cewa masu laifin da suka tuba ba za su koma ga munanan ayyukan baya ba.
Sai dai masana harkokin tsaro sun yi jan hankali, suna cewa bai kamata a mayar da hankali ga tallafawa ʓan bindiga kawai ba.
Dokta Kabiru Adamu, Ęwararre a fannin tsaro, ya bayyana cewa ya kamata a fi karkatar da irin wannan tallafi zuwa ga alāummomin da matsalar ta shafa kai tsaye.
A cewarsa, akwai alāummomin da suka rasa shanu, dukiyoyi, da āyan uwa sakamakon hare-haren Ę“an bindiga, don haka su ne suka fi bukatar tallafin gwamnati.
Ya kuma yi gargadi cewa rarraba tallafi kai tsaye ga Ę“an bindiga na iya Ęara musu Ęwarin guiwa, har ma ya zama kamar an ba su lada saboda aikata laifi.
āBa duka yan bindigan suka shiga ne saboda Ęuncin rayuwa ba. A cikinsu akwai waÉanda suka mayar da sata da garkuwa da mutane sanaāa,ā in ji shi.
Matakin gwamnatin Katsina na zuwa ne bayan wasu alāummomin jihar sun shiga tattaunawar sulhu da yan bindiga.
Duk da haka, rahotanni sun nuna cewa sulhun bai dakatar da hare-haren yan bindiga a wasu jihohin da ke makwabtaka da Katsina ba, inda har yanzu ake fuskantar matsaloli na tsaro.

















