• Latest
  • Trending
  • All
  • News
  • Politics
Jaruman Kannywood da suka rasu a 2024

Jaruman Kannywood da suka rasu a 2024

January 4, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

February 23, 2026
PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

February 22, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

February 19, 2026
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

January 9, 2026
AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in  Quarter-Final

AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in Quarter-Final

January 9, 2026
Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

January 9, 2026
Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

January 8, 2026
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
Monday, March 2, 2026
  • Login
NgHausa
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgHausa
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Blog

Jaruman Kannywood da suka rasu a 2024

by NgHausa
January 4, 2025
in Blog
0
Jaruman Kannywood da suka rasu a 2024
491
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Har yanzu masana’antar Kannywood da masu bibiyarta suna jimamin rasuwar fitaccen mawaƙi El-Mu’az Birniwa, wanda ya rasu a daren Laraba, 4 ga Disamban 2024 a Kaduna.

Rasuwar El-Mu’az ta yi matuƙar girgiza masana’antar Kannywood da ma masoyansa. Hakan ya faru ne saboda yanayin mutuwarsa ta fuju’a, wanda ke sanya jimami ya ɗauki lokaci sosai, musamman ma idan irin wannan mutuwar ta farat-ɗaya ce.

El-Mu’az ya shiga jerin fitattun ‘yan masana’antar da suka yi rasuwar fuju’a, irin su Saratu Daso, Mustapha Waye, da darakta Aminu S. Bono. Wadannan mutane sun bar ƙaƙƙarfan gurbin da ba za a manta da shi ba.

Rasuwar wasu fitattun ‘yan Kannywood a 2024

A ƙarewar shekarar 2024, rahotanni sun tattara sunayen wasu fitattun jarumai da suka rasu cikin shekarar, waɗanda suka bar babban gibi a masana’antar. Ga su kamar haka:

See also  Funtua: Jama’a Na Cikin Fargaba Saboda Hare-Haren ’Yan Bindiga

Fatima Sa’id (Bintu Dadin Kowa)

A ranar Lahadi, 11 ga Fabrairun 2024, jaruma Fatima Sa’id, wadda aka fi sani da Bintu Dadin Kowa, ta rasu. Jarumar ta yi fice a shirin Dadin Kowa na tashar Arewa24, inda aka yaba nata saboda natsuwarta da ƙwarewarta a aikinta. Ta rasu ne sakamakon rashin lafiya, kuma mutuwarta ta girgiza abokan aikinta da masoyanta.

Saratu Giɗaɗo (Saratu Daso)

Ita ma Saratu Giɗaɗo, wadda aka fi sani da Saratu Daso, ta rasu ne a ranar Laraba, 9 ga Afrilu, bayan ta kammala shirye-shiryen sallah. An yi sahur da ita, amma ta rasu a safiyar ranar.

Daso ta shahara a masana’antar Kannywood wajen taka rawar gani a finafinai da kuma yin barkwanci. Mutuwarta ta fuju’a ta yi matuƙar girgiza masana’antar da masoyan finafinan Hausa a duniya.

See also  Hukumar EFCC reshen Kano ta cafke fitacciyar ƴar TikTok, Murja Ibrahim Kunya, bisa zargin yin liƙi da kuɗin Najeriya.

Fatima Usman (Fati Slow Motion)

Tsohuwar jaruma Fatima Usman, wadda aka fi sani da Fati Slow Motion, ta rasu a watan Mayu 2024 a yankin Ouaddai na ƙasar Chadi, kuma a can aka binne ta. Duk da cewa ba ta yawan fitowa a finafinai a lokacin rasuwarta, amma ta yi suna a shekarun farko-farko na habbakar Kannywood. A baya-bayan nan, ta shahara a shafukan sada zumunta, inda ta bar kalmar da ta fi amfani da ita – kebura.

Sulaiman Alaqa

A ranar 22 ga watan Yuli 2024, jarumin Kannywood Sulaiman Alaqa ya rasu. Shi ne mahaifin jarumar Dadin Kowa, Bintalo. Duk da cewa ba ya cikin jaruman da suka yi fice sosai, ya taka rawar gani wajen gina masana’antar tun yana matashi.

See also  Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad

El-Mu’az Muhammad Birniwa

Mawaƙi El-Mu’az Birniwa, wanda ya fito daga jihar Jigawa amma ya yi rayuwa a Kaduna, ya rasu ne yayin shagulgulan taya abokinsa, Auta Waziri, murnar aure. A cewar masoyansa, babban abin da ya dame shi kafin rasuwarsa shi ne rashin cika alkawari. Rasuwar El-Mu’az ta ƙara bayyana rashin tabbas na rayuwa, inda ta bar ‘yan masana’antar cikin baƙin ciki mai tsanani.

Wannan shekarar ta kasance mai ɗauke da babban rashi a masana’antar Kannywood. Wadannan fitattun jarumai da mawaƙa sun bar babban gurbi da za a dade ana jin rashin su.

Allah ya jikansu da rahama.

Share this:

  • Share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Share on X (Opens in new window) X
Share196Tweet123Share49
NgHausa

NgHausa

NgHausa

Copyright © 2017 JNews.

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

Copyright © 2017 JNews.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks