• Latest
  • Trending
  • All
Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”

Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”

July 1, 2025
Nnamdi Kanu Ya Amince Zai Tuntubi Lauyoyinsa Kafin Ya Fara Kare Kansa

Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi

November 20, 2025
ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

November 20, 2025
NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

November 17, 2025
Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

November 15, 2025
Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

November 13, 2025
Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

November 12, 2025
Matsalar Tsaro a Kano: 'Yan sa kai na ƙauyen Shanono suna sintiri domin kare al’umma daga harin ƴan bindiga.

Matsalar Tsaro a Kano: ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Faruruwa, Sun Yi Garkuwa da Mata Biyar

November 12, 2025
NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

November 11, 2025
Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

November 11, 2025
Tsohon Gwamnan Rivers Nyesom Wike tare da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Alkali James Omotosho yayin rikicin siyasa na dokar ta-baci a Jihar Rivers, Najeriya, 2025.

Rikicin Siyasar Jihar Rivers: Wike, Tinubu, da Alkali James Omotosho

November 11, 2025
Dharmendra Ya Kwantar da Hankalin Masoyansa Bayan Shiga Asibiti

Dharmendra Ya Kwantar da Hankalin Masoyansa Bayan Shiga Asibiti

November 10, 2025
Farkon Shirin Super Eagles Don Wasan Takarar Karshe Na Fifa World Cup 2026 a Rabat

Farkon Shirin Super Eagles Don Wasan Takarar Karshe Na Fifa World Cup 2026 a Rabat

November 10, 2025
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
Friday, November 21, 2025
NgHausa News
  • Login
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
No Result
View All Result
NgHausa News
No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
🚀 Join Our Telegram Community

Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”

by NgHausa
July 1, 2025
in KannyWood
0
Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”
0
SHARES
23
VIEWS

Daya daga cikin fitattun furodusoshin Kannywood, Abubakar Bashir Maishadda, ya bayyana manyan burikansa da irin nasarorin da ya gani a cikin masana’antar fina-finai. Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da Hadiza Gabon a cikin shirin ta na “Gabon’s Room Talk Show.”

A cikin hirar, Maishadda ya tabo batutuwa da dama – daga burin sa a masana’antar, har zuwa albarkar da ya ce tana cikin harkar fina-finai idan aka yi amfani da ita yadda ya dace.

“Idan ka samu kanka a cikin wannan masana’anta ba tare da ka amfana da romon arzikin da Allah ya ajiye a cikinta ba, to guda biyu ne: ko dai dama ta zo maka amma ba ka amfana da ita yadda ya kamata ba, ko kuma ba ka yi abin da ya dace ba a lokacin da ya dace,” in ji Maishadda, wanda ya shafe fiye da shekaru 15 yana daukar nauyin fina-finai.

Dalilin da ya hana shi halartar bikin Rarara da Aisha Humaira

Da yake amsa tambaya kan dalilin da ya sa ba a gan shi a bikin daurin auren mawaki Dauda Kahutu Rarara da Amaryarsa, Aisha Humaira, Maishadda ya ce tafiya zuwa birnin Legas ce ta hana shi halartar taron.

“Bikin Rarara da Aisha Humaira, tamu ce. A gaskiya ni ne sanadin haduwarsu tun da fari. Mun taba yin waka tare da Rarara inda na dauki nauyin wakar. Bayan mun kammala, na bukaci a yi reposting a dandalin sada zumunta. Aisha Humaira na daga cikin wadanda suka yi hakan,” in ji shi.

Ya kara da cewa wannan damar ce ta bude kofar hadin gwiwa tsakaninsu.

“Na nuna wa Rarara irin yadda ta dage wajen yada wakar. Sai na bukaci a sanya ta a wata waka da muka shirya, domin a lokacin kamar kawata ce. Daga nan muka yi wakar ‘Dogara Ya Dawo’ tare.”

Alaƙarsa da Umar M. Sharif

Dangane da jita-jitar da ke yawo cewa alakar Maishadda da mawaki/actor Umar M. Sharif ta tabarbare, ya bayyana cewa ba gaskiya ba ce.

“Ba a ganin Umar a cikin ‘Gidan Sarauta’ zango na hudu ba yana nufin akwai matsala. A shirye-shirye masu dogon zango, sau da yawa ana cire jarumai sannan daga baya su dawo. Don haka babu wata matsala a tsakanina da Umar,” in ji Maishadda.

Yaushe aure da Nana Firdausi?

Ana ta rade-radin cewa yana da niyyar aure da jarumar fina-finai Nana Firdausi, duba da yadda suke yawan fitowa a fina-finai tare.

“Eh, muna aiki da juna sosai. Na yarda da kwazonta. Duk wani aiki da muka yi tare, tana nuna cikakken hazaka da kishin aiki. Amma har yanzu babu wani batu na aure a tsakanina da ita. Fahimta ce ke tsakaninmu,” in ji shi.

Burin Maishadda: Fita da Kannywood zuwa duniya

Maishadda ya bayyana babban burinsa a yanzu da cewa yana fatan ya fitar da fina-finan Kannywood zuwa kasashen waje, musamman India.

“Ina son in zama furodusa na duniya – wato ‘International Producer’. Ba zan tsaya a Najeriya kawai ba. Ina burin yin fim a India, kasar da ake samun riba sosai a harkar fina-finai,” in ji shi.

Ya ce ya riga ya fara gayyatar jaruman kudu kamar Kanayo O. Kanayo don yin aiki tare da su.

“Burin da nake da shi ga wannan masana’anta ba zai mutu ba. In Allah ya bani dama, zan sa Kannywood ta shiga duniya har kowa ya santa.”

Fim ba karamin abu ba ne

Ya ci gaba da cewa harkar fim na dauke da arziki, daukaka, da soyayya daga al’umma.

“Fim na baka suna fiye da yadda kake zato. Wani lokaci ka isa wurare da ko a mafarki ba ka taba tunanin ka isa ba. Gwamna na iya tunanin an san shi a ko’ina, amma haka dan fim ma yake. A karshe dai fim na daga cikin hanyoyin da ke gina mutum.”

Kira ga mutane

A karshe, Maishadda ya shawarci mutane da su daina raina wani, musamman a lokacin da bai kai ko’ina ba.

“A lokacin da na fara wannan sana’a, mutane da dama sun raina ni, sun toshe hanyoyi. Amma yau gashi Allah ya daukaka ni. Abin da ka raina yau, ka iya girmama shi gobe,” in ji Maishadda wanda ake wa lakabi da ‘King of Box Office’ a Kannywood.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X
See also  I am very happy with my role as Mainasara in the Labarina Series.
Join our WhatsApp Channel
Tags: Ali NuhuKannyWoodLabarina
NgHausa

NgHausa

Related Posts

Kannywood Ta Yi Rashi: Fitaccen Jarumi Malam Nata’ala Ya Rasu Bayan Doguwar Jinya

Kannywood Ta Yi Rashi: Fitaccen Jarumi Malam Nata’ala Ya Rasu Bayan Doguwar Jinya

by NgHausa
November 2, 2025
0

Masana’antar Kannywood ta shiga cikin jimami bayan samun labarin rasuwar shahararren jarumi Mato Yakubu, wanda aka fi sani da Malam...

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

by NgHausa
October 29, 2025
0

Kabiru Abubakar Aliyu, wanda aka fi sani da Nakwango, ɗaya daga cikin fitattun dattawan masana’antar Kannywood, ya bayyana yadda ya...

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad

by NgHausa
October 28, 2025
0

Jaruma Khadija Muhammad, wacce ta fito a fina-finai irin su Gidan Sarauta, ta bayyana a fili cewa ba ta shiga...

Kannywood: Masana Na Tunanin Komawa Gidajen Gala Bayan Dogaro da YouTube

Kannywood: Masana Na Tunanin Komawa Gidajen Gala Bayan Dogaro da YouTube

by NgHausa
October 5, 2025
0

Masana Kannywood na tattauna yiwuwar komawa haska finafinai a gidajen gala bayan dogon lokaci suna dogaro da YouTube, domin fadada...

Recent Posts

  • Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi
  • ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba
  • NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya
  • Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa
  • Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Recent Comments

  1. Yusuf tanko on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  2. Abdulazeez jibrin on Yadda Zaka Samu Tallafin Kudi a Najeriya (2025): Matakai da Sharuɗɗa
  3. Bashir Gamzaki on COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 PROF. Isah Ali Ibrahim Pantami
  4. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  5. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”

Archives

  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024

Categories

  • Blog
  • Entertainment
  • Hausa Series
  • KannyWood
  • Labaran Duniya
  • Lafiya
  • Nigeria
  • Nishadi
  • Opportunity
  • Siyasa
  • Sports
  • TAFSEER
  • Wasanni
NgHausa News

© NG Hausa News – 2025

Navigate Site

  • About Us
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood

© NG Hausa News – 2025

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks