• Latest
  • Trending
  • All
  • News
  • Politics
Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”

Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”

July 1, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

February 23, 2026
PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

February 22, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

February 19, 2026
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

January 9, 2026
AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in  Quarter-Final

AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in Quarter-Final

January 9, 2026
Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

January 9, 2026
Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

January 8, 2026
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
Monday, March 2, 2026
  • Login
NgHausa
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgHausa
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Blog

Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”

by NgHausa
July 1, 2025
in Blog
0
Maishadda: “Burin da nake da shi yanzu shi ne na fitar da Kannywood zuwa duniya!”
491
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daya daga cikin fitattun furodusoshin Kannywood, Abubakar Bashir Maishadda, ya bayyana manyan burikansa da irin nasarorin da ya gani a cikin masana’antar fina-finai. Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da Hadiza Gabon a cikin shirin ta na “Gabon’s Room Talk Show.”

A cikin hirar, Maishadda ya tabo batutuwa da dama – daga burin sa a masana’antar, har zuwa albarkar da ya ce tana cikin harkar fina-finai idan aka yi amfani da ita yadda ya dace.

“Idan ka samu kanka a cikin wannan masana’anta ba tare da ka amfana da romon arzikin da Allah ya ajiye a cikinta ba, to guda biyu ne: ko dai dama ta zo maka amma ba ka amfana da ita yadda ya kamata ba, ko kuma ba ka yi abin da ya dace ba a lokacin da ya dace,” in ji Maishadda, wanda ya shafe fiye da shekaru 15 yana daukar nauyin fina-finai.

Dalilin da ya hana shi halartar bikin Rarara da Aisha Humaira

Da yake amsa tambaya kan dalilin da ya sa ba a gan shi a bikin daurin auren mawaki Dauda Kahutu Rarara da Amaryarsa, Aisha Humaira, Maishadda ya ce tafiya zuwa birnin Legas ce ta hana shi halartar taron.

“Bikin Rarara da Aisha Humaira, tamu ce. A gaskiya ni ne sanadin haduwarsu tun da fari. Mun taba yin waka tare da Rarara inda na dauki nauyin wakar. Bayan mun kammala, na bukaci a yi reposting a dandalin sada zumunta. Aisha Humaira na daga cikin wadanda suka yi hakan,” in ji shi.

Ya kara da cewa wannan damar ce ta bude kofar hadin gwiwa tsakaninsu.

“Na nuna wa Rarara irin yadda ta dage wajen yada wakar. Sai na bukaci a sanya ta a wata waka da muka shirya, domin a lokacin kamar kawata ce. Daga nan muka yi wakar ‘Dogara Ya Dawo’ tare.”

Alaƙarsa da Umar M. Sharif

Dangane da jita-jitar da ke yawo cewa alakar Maishadda da mawaki/actor Umar M. Sharif ta tabarbare, ya bayyana cewa ba gaskiya ba ce.

“Ba a ganin Umar a cikin ‘Gidan Sarauta’ zango na hudu ba yana nufin akwai matsala. A shirye-shirye masu dogon zango, sau da yawa ana cire jarumai sannan daga baya su dawo. Don haka babu wata matsala a tsakanina da Umar,” in ji Maishadda.

Yaushe aure da Nana Firdausi?

Ana ta rade-radin cewa yana da niyyar aure da jarumar fina-finai Nana Firdausi, duba da yadda suke yawan fitowa a fina-finai tare.

“Eh, muna aiki da juna sosai. Na yarda da kwazonta. Duk wani aiki da muka yi tare, tana nuna cikakken hazaka da kishin aiki. Amma har yanzu babu wani batu na aure a tsakanina da ita. Fahimta ce ke tsakaninmu,” in ji shi.

Burin Maishadda: Fita da Kannywood zuwa duniya

Maishadda ya bayyana babban burinsa a yanzu da cewa yana fatan ya fitar da fina-finan Kannywood zuwa kasashen waje, musamman India.

“Ina son in zama furodusa na duniya – wato ‘International Producer’. Ba zan tsaya a Najeriya kawai ba. Ina burin yin fim a India, kasar da ake samun riba sosai a harkar fina-finai,” in ji shi.

Ya ce ya riga ya fara gayyatar jaruman kudu kamar Kanayo O. Kanayo don yin aiki tare da su.

“Burin da nake da shi ga wannan masana’anta ba zai mutu ba. In Allah ya bani dama, zan sa Kannywood ta shiga duniya har kowa ya santa.”

Fim ba karamin abu ba ne

Ya ci gaba da cewa harkar fim na dauke da arziki, daukaka, da soyayya daga al’umma.

“Fim na baka suna fiye da yadda kake zato. Wani lokaci ka isa wurare da ko a mafarki ba ka taba tunanin ka isa ba. Gwamna na iya tunanin an san shi a ko’ina, amma haka dan fim ma yake. A karshe dai fim na daga cikin hanyoyin da ke gina mutum.”

Kira ga mutane

A karshe, Maishadda ya shawarci mutane da su daina raina wani, musamman a lokacin da bai kai ko’ina ba.

“A lokacin da na fara wannan sana’a, mutane da dama sun raina ni, sun toshe hanyoyi. Amma yau gashi Allah ya daukaka ni. Abin da ka raina yau, ka iya girmama shi gobe,” in ji Maishadda wanda ake wa lakabi da ‘King of Box Office’ a Kannywood.

Share this:

  • Share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Share on X (Opens in new window) X
See also  Goodluck Jonathan 2027: Muhawara kan kundin tsarin mulkin Najeriya
Tags: Ali NuhuKannyWoodLabarina
Share196Tweet123Share49
NgHausa

NgHausa

NgHausa

Copyright © 2017 JNews.

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

Copyright © 2017 JNews.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks