• Latest
  • Trending
  • All
Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi

Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi

February 2, 2025
Gwamnatin Jihar Niger Ta Daura wa Makarantar St. Mary Alhakin Sace Dalibai

Gwamnatin Jihar Niger Ta Daura wa Makarantar St. Mary Alhakin Sace Dalibai

November 21, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Makarantar Kwana a Jihar Niger, Sun Sace Dalibai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Makarantar Kwana a Jihar Niger, Sun Sace Dalibai

November 21, 2025
Babbar Kotun Tarayya Ta Yanke Wa Nnamdi Kanu Hukuncin Daurin Rai Da Rai

Babbar Kotun Tarayya Ta Yanke Wa Nnamdi Kanu Hukuncin Daurin Rai Da Rai

November 21, 2025
Nnamdi Kanu Ya Amince Zai Tuntubi Lauyoyinsa Kafin Ya Fara Kare Kansa

Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi

November 20, 2025
ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

November 20, 2025
NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

November 17, 2025
Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

November 15, 2025
Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

November 13, 2025
Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

November 12, 2025
Matsalar Tsaro a Kano: 'Yan sa kai na ƙauyen Shanono suna sintiri domin kare al’umma daga harin ƴan bindiga.

Matsalar Tsaro a Kano: ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Faruruwa, Sun Yi Garkuwa da Mata Biyar

November 12, 2025
NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

November 11, 2025
Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

November 11, 2025
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
Sunday, December 7, 2025
NgHausa News
  • Login
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
No Result
View All Result
NgHausa News
No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
🚀 Join Our Telegram Community

Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi

by NgHausa
February 2, 2025
in KannyWood
0
Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi
0
SHARES
2.7k
VIEWS

Faiza Abdullahi, jarumai dake fitowa a matsayin matar Kofur Audu a shirin Dadin Kowa, ta bayyana haka ne ga mujallar film a lokacin tattaunawar ta da wakilin ta.

Mu fara da jin tarihin rayuwar ki.


FA’IZA: Na farko, suna na Fa’iza Abdullahi. An haife ni ne a cikin Jihar Bauchi, a wani gari da ake kira Jalaf a Ƙaramar Hukumar Damban. A can na yi karatu na girma duk a can. A yanzu dai ban wuce shekara 26 ba, sai kuma a yanzu da na kasance a garin Kano ina gudanar da sana’a ta ta aikin fim.

Shin fim ne ya kawo ki Kano kuma a wane lokacin kika zo?


FA’IZA: To gaskiya, zuwa na Kano zai kai shekara bakwai a yanzu kuma harkar fim ce ta kawo ni Kano, don in ban da ta dalilin fim ban san kowa a Kano ba, ban ma taɓa zuwa ba sai ta sanadin zan yi fim.

Da yake an fi sanin Fa’iza Abdullahi a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’ a matsayin matar Kofur Audu, ko kin taɓa yin wani fim ɗin kafin ki fara ‘Daɗin Kowa’?

See also  Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango


FA’IZA: Gaskiya ban taɓa yin wani fim ba sai ‘Daɗin Kowa’, don da shi na fara. Ba zan manta ba lokacin da na zo garin Kano haka, ina zuwa Zoo Road akwai wani da na sani wanda shi ne darakta a fim ɗin a lokacin, nakan je na gaishe su, duk da ban ma san shi waye ba a lokacin, sai wata rana ya kira ni ya ce na zo ana nema na zan yi sin ɗaya a wani aiki, to ban ma san yadda abin yake ba sai da na je. To da haka na fara, har aka zo daga baya ake kira na lokaci zuwa lokaci. Kuma lokacin da na fara fitowa a cikin ‘Daɗin Kowa’, a matsayin ‘yar tuwo-tuwo ce mai sayar da abinci, kuma ba mu da gida, ni kaɗai ce a wajen abinci sai masu zuwa su saya.

See also  Rashinsa: Tasirin Rabilu Musa Ibro a Kannywood

Shin akwai bambanci tsakanin rayuwar Fa’iza Abdullahi ta zahiri da kuma ta shirin ‘Daɗin Kowa’?


FA’IZA: To akwai bambanci sosai, saboda ka ga dai ita Fa’iza Abdullahi a zahiri ba ta faɗa, sannan tana girmama na gaba da ita da sauran abubuwa na girmamawa. Amma ita Bilkisu a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’ ba ta da kunya, ba mu’amala mai kyau, ko gidan su ma ba ta girmama su ba. Haka gidan mijin ta ma ba ta raga wa kowa ba. To amma sai ya kasance mutane a gari suna kallo na a matsayin Bilkisu maimakon su kalle ni a matsayin Fa’iza Abdullahi. Da yawa abin da na fi fuskanta a rol ɗin da nake, sai mutane idan mun haɗu su rinƙa cewa Allah ya ƙara. Abin da nake yi wa Kofur Audu suna jin daɗi saboda macuci ne azzalumi. Wasu kuma suna cewa bai kamata ba, na rinƙa sassauta masa.

See also  Kannywood: Masana Na Tunanin Komawa Gidajen Gala Bayan Dogaro da YouTube

Wane rol kika fi so a saka ki?


FA’IZA: Gaskiya duk da a cikin fim babu rol ɗin da ba na takawa, na fi so a saka ni na fito a masifaffiyar mace. Ina son na fito na yi masifa yadda rai na yake so. Don ka ga ko rol ɗin da nake yi a yanzu a cikin fim ɗin ‘Muhalli’ wani rol ne da na fito a matsayin matar aure amma marar mutunci, masifaffiya. Don haka ina son rol ɗin sosai na fito a matar aure marar mutunci, marar tarbiyya. Don haka nake son rol ɗin, don an ba ni dama ina yin masifa yadda rai na yake so, kuma ga ni matar mai kuɗi, ina jin daɗin rayuwa, ga kuma ina zuba masifa. Don haka ina jin daɗi sosai da wannan rol ɗin.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X
Join our WhatsApp Channel
NgHausa

NgHausa

Related Posts

Kannywood Ta Yi Rashi: Fitaccen Jarumi Malam Nata’ala Ya Rasu Bayan Doguwar Jinya

Kannywood Ta Yi Rashi: Fitaccen Jarumi Malam Nata’ala Ya Rasu Bayan Doguwar Jinya

by NgHausa
November 2, 2025
0

Masana’antar Kannywood ta shiga cikin jimami bayan samun labarin rasuwar shahararren jarumi Mato Yakubu, wanda aka fi sani da Malam...

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

by NgHausa
October 29, 2025
0

Kabiru Abubakar Aliyu, wanda aka fi sani da Nakwango, ɗaya daga cikin fitattun dattawan masana’antar Kannywood, ya bayyana yadda ya...

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad

by NgHausa
October 28, 2025
0

Jaruma Khadija Muhammad, wacce ta fito a fina-finai irin su Gidan Sarauta, ta bayyana a fili cewa ba ta shiga...

Kannywood: Masana Na Tunanin Komawa Gidajen Gala Bayan Dogaro da YouTube

Kannywood: Masana Na Tunanin Komawa Gidajen Gala Bayan Dogaro da YouTube

by NgHausa
October 5, 2025
0

Masana Kannywood na tattauna yiwuwar komawa haska finafinai a gidajen gala bayan dogon lokaci suna dogaro da YouTube, domin fadada...

Recent Posts

  • Gwamnatin Jihar Niger Ta Daura wa Makarantar St. Mary Alhakin Sace Dalibai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Makarantar Kwana a Jihar Niger, Sun Sace Dalibai
  • Babbar Kotun Tarayya Ta Yanke Wa Nnamdi Kanu Hukuncin Daurin Rai Da Rai
  • Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi
  • ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

Recent Comments

  1. Yusuf tanko on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  2. Abdulazeez jibrin on Yadda Zaka Samu Tallafin Kudi a Najeriya (2025): Matakai da Sharuɗɗa
  3. Bashir Gamzaki on COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 PROF. Isah Ali Ibrahim Pantami
  4. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  5. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”

Archives

  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024

Categories

  • Blog
  • Entertainment
  • Hausa Series
  • KannyWood
  • Labaran Duniya
  • Lafiya
  • Nigeria
  • Nishadi
  • Opportunity
  • Siyasa
  • Sports
  • TAFSEER
  • Wasanni
NgHausa News

© NG Hausa News – 2025

Navigate Site

  • About Us
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood

© NG Hausa News – 2025

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks