• Latest
  • Trending
  • All
  • News
  • Politics
Nusaiba Muhammad Ibrahim smiling during an interview

Tattaunawa da Nusaiba Muhammad Ibrahim (Sailuba)

August 3, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

February 23, 2026
PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

February 22, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

February 19, 2026
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

January 9, 2026
AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in  Quarter-Final

AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in Quarter-Final

January 9, 2026
Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

January 9, 2026
Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

January 8, 2026
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
Monday, March 2, 2026
  • Login
NgHausa
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgHausa
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Blog

Tattaunawa da Nusaiba Muhammad Ibrahim (Sailuba)

by NgHausa
August 3, 2025
in Blog
0
Nusaiba Muhammad Ibrahim smiling during an interview

Nusaiba Muhammad

491
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Shafin Rumbun Nishadi ya zanta da daya daga cikin fitattun jaruman Kannywood masu tasowa, Nusaiba Muhammad Ibrahim, wacce aka fi sani da Sailuba a cikin shirin Dadin Kowa. A cikin hirar, ta bayyana yadda ta fara harkar fim, irin nasarorin da ta samu, da kuma shawarwarinta ga matasa da ke sha’awar shiga masana’antar.

Cikakken Sunanta da Takarar Rayuwa

Tambaya: Za ki iya bayyana cikakken sunanki da kuma sunan da aka fi sanin ki da shi?

Amsa: Sunana Nusaiba Muhammad Ibrahim, amma yawanci ana kirana da Sailuba Dadin Kowa.

Tambaya: Za ki gaya mana takaitaccen tarihin rayuwarki?

Amsa: An haife ni a Gombe, amma na koma Kano tun ina ‘yar shekara biyar saboda aikin mahaifina. Na yi karatuna na firamare da sakandare a Kano. Har yanzu ni budurwa ce, ba auren na yi ba.

Farkon Shiga Fim da Kalubale

Tambaya: Yaya kika fara harkar fim?

Amsa: Fim ya burge ni tun da daɗe. Na fara sha’awar shiga ne bayan na kalli wani fim da ya kunshi sakon da ya shafi gyaran rayuwa. Wannan ne ya ƙarfafa min gwiwa.

See also  SADIQ SANI SADIQ YA CACCAKI MASU CEWA YAN FILM SUNA KOYAR DA TARBIYA

Tambaya: Shin kin fuskanci ƙalubale daga iyaye?

Amsa: Eh, a farko sun nuna damuwa, amma daga baya sun fahimce ni. Iyaye na masu fahimta ne.

Tambaya: Wa ya taimaka miki shiga masana’antar?

Amsa: Wani É—an fim ne ya taimaka, wanda kuma muka taso tare a unguwa. Iyayensa da nawa sun saba sosai.

Ayyukan da Ta Yi da Kwarewarta

Tambaya: Wane fim kika fara da shi?

Amsa: Na fara ne da fim ɗin Dadin Kowa inda na fito a matsayin Sailuba – matar aure da surukarta ta samo mata miji daga kauye.

Tambaya: Wane fim ya fi haskaka ki a idon jama’a?

Amsa: Dadin Kowa da Matar Waye sun fi nuna fasahar da nake da ita.

Tambaya: Wadanne wasu fina-finai kika fito ciki?

Amsa: Na fito a fina-finai kamar Ni da Mijin Yayata, Zaman Tare, Matar Kaddara da sauransu.

Nasara da Darussa

Tambaya: Me kika samu ta hanyar harkar fim?

See also  Biden discussed with Tinubu the need to release the Binance employee

Amsa: Alhamdulillah, na samu abubuwa da dama kamar kudi, motar hawa, kaya da kayan kamshi.

Tambaya: Ko kina da manyan mutanen da ke mara miki baya a masana’antar?

Amsa: E, akwai kamar su Adam Musa Adam da Usman Adam (Hali Dubu).

Tambaya: Wane fim ya fi burge ki?

Amsa: Ni da Mijin Yayata ya fi burge ni saboda na taka rawa mai ban sha’awa a ciki.

Rayuwa a Bayan Fim

Tambaya: Yaya mutanen unguwarku suka karɓe ki bayan kin bayyana a fim?

Amsa: Da dama sun nuna mamaki, wasu har sun ce sun fi ganina a fim fiye da a zahiri. Wasu kuma sun yi mamakin kyawun da suke gani a wajen fim.

Tambaya: Ko kin fuskanci wata matsala daga masu kallo?

Amsa: A’a. Sai dai wasu su nuna mamaki idan suka gan ni a zahiri.

Rayuwar Aure da Shawarwari

Tambaya: Yaushe kike sa ran yin aure?

Amsa: Duk lokacin da Allah ya kawo lokaci, a shirye nake.

Tambaya: Wane irin namiji kike so?

See also  Mansura Isah Ta Bayyana Yadda tsohon mijinta ya sake ta bayan Æ™wace mata kwangilar biliyoyin naira da yayi

Amsa: Musulmi ne mai tarbiyya, ilimi da sana’a mai kyau.

Tambaya: Ko za ki iya auren jarumin fim?

Amsa: E mana. In har ya cancanta, ba matsala.

Shawarwari ga Matasa da Masu Sha’awar Fim

Tambaya: Wace shawara za ki ba abokan aikinki?

Amsa: Mu hada kai, mu kare mutuncinmu da na sana’armu. Kada mu bari wani abu ya bata mana suna.

Tambaya: Wace shawara za ki ba masu sha’awar shiga fim?

Amsa: Su shiga da niyya mai kyau. Su fahimci cewa fim sana’a ce da ke da daraja.

Tambaya: Ko kina da gaisuwa?

Amsa: Ina gaida dukan masoyana, da masu kallon fina-finai na. Ina rokon alheri a gare su.

Ƙarshe

Wannan tattaunawa ta bayyana gaskiya da himma a zuciyar Nusaiba Muhammad Ibrahim wajen ci gaba da haskakawa a masana’antar Kannywood. Tabbas, tana daya daga cikin matan da ke kawo sauyi a fagen fim a yau.

Share this:

  • Share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Share on X (Opens in new window) X
Share196Tweet123Share49
NgHausa

NgHausa

NgHausa

Copyright © 2017 JNews.

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

Copyright © 2017 JNews.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks