Labaran Duniya

Dalibin BUK Ya Rasa Ransa Bayan Harin Masu Kwacen Waya a Kano

Umar Abdullahi Hafizi, dalibin buk a shekarar ƙarshe mai karatun Sociology a Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), ya rasa ransa sakamakon harin da wasu da ake zargin ‘yan ƙwacen waya ne suka kai masa.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na dare a ranar Talata, a unguwar Dorayi da ke Ƙaramar Hukumar Gwale, Jihar Kano.

Yadda Lamarin Ya Faru

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun soka Umar da wuka, sannan suka tsere da wayarsa. Bayan an garzaya da shi asibiti, ya rasu sakamakon munanan raunukan da ya samu.

See also  Yadda Ake Duba Sakamakon WAEC a 2025

Martanin Jami’a da Hukumomi

Jami’ar BUK ta tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai, Malam Lamara Garba, ya fitar. Sanarwar ta nuna jimamin jami’ar tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayin, abokansa da sauran ɗalibai.

Shugaban jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya ce jami’ar na aiki tare da hukumomin tsaro domin kama masu laifin.

An Yi Jana’iza a Zariya

An binne marigayin a garinsu da ke Zariya, Jihar Kaduna. Jami’ar ta buƙaci ɗalibai da su kwantar da hankalinsu, tare da kasancewa masu lura da lafiyar kansu da muhallinsu.

Haka kuma, an buƙaci jama’a da su taimaka da duk wani bayani da zai iya taimakawa jami’an tsaro wajen gano masu laifin.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Enable Notifications OK No thanks