• Latest
  • Trending
  • All
Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

September 25, 2025
Nnamdi Kanu Ya Amince Zai Tuntubi Lauyoyinsa Kafin Ya Fara Kare Kansa

Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi

November 20, 2025
ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba

November 20, 2025
NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya

November 17, 2025
Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa

November 15, 2025
Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

November 13, 2025
Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

Ba zan bari a gina filin da ba shi da takardu ba – Ministan Abuja Wike

November 12, 2025
Matsalar Tsaro a Kano: 'Yan sa kai na ƙauyen Shanono suna sintiri domin kare al’umma daga harin ƴan bindiga.

Matsalar Tsaro a Kano: ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari a Faruruwa, Sun Yi Garkuwa da Mata Biyar

November 12, 2025
NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

NYSC Ta Fitar da Lambobin Kira Ga Mambobin Batch C Na 2025

November 11, 2025
Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

Rikicin Nyesom Wike da Sojojin Najeriya: Abin da ya faru a Abuja

November 11, 2025
Tsohon Gwamnan Rivers Nyesom Wike tare da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Alkali James Omotosho yayin rikicin siyasa na dokar ta-baci a Jihar Rivers, Najeriya, 2025.

Rikicin Siyasar Jihar Rivers: Wike, Tinubu, da Alkali James Omotosho

November 11, 2025
Dharmendra Ya Kwantar da Hankalin Masoyansa Bayan Shiga Asibiti

Dharmendra Ya Kwantar da Hankalin Masoyansa Bayan Shiga Asibiti

November 10, 2025
Farkon Shirin Super Eagles Don Wasan Takarar Karshe Na Fifa World Cup 2026 a Rabat

Farkon Shirin Super Eagles Don Wasan Takarar Karshe Na Fifa World Cup 2026 a Rabat

November 10, 2025
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
Friday, November 21, 2025
NgHausa News
  • Login
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
No Result
View All Result
NgHausa News
No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood
🚀 Join Our Telegram Community

Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

by NgHausa
September 25, 2025
in Blog
0
Tantance Wa’azi a Kano: Rikicin Kalaman Malamai da Bukatar Sabon Doka

Kano State

0
SHARES
32
VIEWS

Rikicin Kalaman Malamai da Batun Dokar Tantance Wa’azi a Kano

Faruwar al’amura masu alaƙa da addini da kuma yadda suke jawo tarzoma a Kano na ƙara jefa tambayoyi: shin akwai buƙatar samar da dokokin da za su kula da wa’azi a jihar?

A ranar Larabar da ta gabata, dubban mazauna Kano sun gudanar da zanga-zangar lumana zuwa gidan gwamnati, suna ƙorafi kan zargin kalaman da suka kira “rashin ladabi” ga Annabi Muhammadu (SAW).

Wannan ba shi ne karo na farko da ake samun irin waɗannan cece-kuce ba. A lokuta da dama, ana samun zarge-zargen da ke jawo muƙabala tsakanin malamai ko kuma cin gaban shari’a a kotu.

A makon da ya gabata ma, gwamnatin jihar Neja ta sanar da shirin tantance hudubar malamai da limaman coci. Ta bayyana cewa manufar hakan ita ce dakile kalaman da kan iya tunzura jama’a. Sai dai abin tambaya a nan shi ne: ko Kano ma na buƙatar irin wannan doka?

Me Ya Faru a Kano?

A ranar Laraba, wasu mazauna birnin Kano sun gudanar da zanga-zangar lumana kan zargin cewa Sheikh Lawan Abubakar Triumph ya yi kalaman da ba su dace ba game da Annabi Muhammadu (SAW).

Masu zanga-zangar sun taru a kofar gidan gwamnati, inda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓe su tare da yin jawabi.

A wani bidiyo da ya yaɗu a baya-bayan nan, an ga malamin yana musanta labarin cewa haihuwar Annabi Muhammadu da shayinsa wani abin al’ajabi ne. A cewarsa, ba karama ba ce, domin ana iya samun irin hakan a haihuwar sauran mutane. Ya ƙara da cewa ruwayoyin da ke nuna hakan ba su da inganci.

See also  Amaryar TikTok Ta Fadi Matsalar da Jaruman Kannywood ke Fuskanta

Martanin Gwamnan Kano

ɗalibai a aji suna murna bayan NECO 2025 yayin da Jihar Kano ta bayyana nasarar yawan masu cin jarabawa.
Abba Kabir Yusuf

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umarci masu zanga-zangar da su kwantar da hankali. Ya roƙe su da su rubuta takardar koke a hukumance ta hannun ofishin sakataren gwamnati.

“In Allah ya yarda, za mu ɗauki matakin da bai saba wa Shari’a ba,” in ji shi.

Gwamnan ya ƙara da cewa: “Ku rubuta takarda ta hukumance, ita ce za mu yi amfani da ita daga nan har zuwa ƙolin ƙoli.”

Masu ƙorafin sun amince za su gabatar da takardar da misalin ƙarfe 10:00 na safiyar Alhamis.

Ra’ayin Malamai a Kano

BBC ta tuntubi wasu malamai guda biyu a Kano. Duk da sun buƙaci a sakaya sunayensu, sun bayyana ra’ayoyi mabambanta.

Malami na farko ya ce:
“Tuni ya kamata gwamnati ta samar da doka ta wa’azi domin tantance abin da ya dace da abin da bai dace ba. Haka kuma ya kamata a fayyace akan wace mazhaba malaman Kano za su koya, tare da tantance littafan da ake amfani da su.”

Sai dai wani malami daban ya yi adawa da hakan:
“Babu buƙatar gwamnati ta shiga harkar malamai. Idan hakan ta faru, siyasa za ta shigo. Kuma idan malami bai goyi bayan gwamnati ba, za a iya ɗaukar matakin hukunta shi. Amma gaskiya malamai suna sakin baki fiye da kima, suna rikita fahimtar jama’a.”

See also  Rarara Builds Three Primary Schools In Katsina State

Abin da NSCIA Ta Bukata

A watan Fabrairu 2025, Majalisar Ƙoli ta Harkokin Shari’ar Musulunci a Najeriya (NSCIA), ƙarƙashin Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III, ta yi kira da a samar da dokokin da za su tantance masu wa’azi a faɗin ƙasa.

Bayan taro, Sakatare Janar na Jama’atu Nasril Islam (JNI), Farfesa Khalid Aliyu, ya bayyana cewa lokaci ya yi a tsara wa’azi:

“Kar a mayar da minbarin tafsiri wurin habaici da zage-zage. Wa’azi ya kamata ya kasance bisa ilimi da gaskiya, ba kwaikwayo a gaban kyamara kawai ba.”

Shi ma wani sakatare, Malam Nafi’u Baba-Ahmed, ya ce:
“Wajibi ne gwamnati ta samar da dokoki da za su tsara wa’azi da tafsiri. Yanzu haka, wasu suna fitowa suna magana bisa jahilci suna kira kansu malamai.”

Me Kundin Tsarin Mulki Ya Ce?

Lauya mai zaman kansa a Kano, Barista Sulaiman Magashi, ya bayyana cewa tsarin mulki ya yarda mutum ya yi wa’azi, amma hakan ba ya nufin a yi shi ba tare da tsari ba.

“Akwai buƙatar a tsara wa’azi, domin shi ma sana’a ce wadda shari’ar Musulunci da tsarin ƙasa suka amince da ita. Amma ba a ba wa kowa dama ya yi amfani da wa’azi wajen tayar da tarzoma ko cin mutunci ba,” in ji shi.

See also  Trump Attends the Return of the Remains of the Navy SEAL Who Died in Yemen

Sai dai ya ja kunne cewa, idan aka yi irin wannan doka, ya zama wajibi a saka masu ruwa da tsaki ciki, tare da guje wa siyasa ko nuna bambanci.

Lokutan Da Kalaman Malamai Suka Tunzura Kano

  • Yuli 2025: Rundunar ƴansandan Kano ta gayyaci Sheikh Lawal Triumph bayan wasu sun nemi a halatta jininsa saboda zargin kalaman rashin ladabi ga Annabi (SAW). Rikicin ya kusan jefa jihar cikin tashin hankali.
  • Yuli 2021: Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara ya fuskanci zarge-zargen batanci ga Annabi (SAW). Rikicin ya haifar da muƙabala da shari’a, wanda daga ƙarshe aka yanke masa hukuncin kisa.

Rikice-rikicen da suka shafi malamai a Kano na ƙara ƙarfafa muhawara kan ko ya dace gwamnati ta kafa doka ta musamman don tsara wa’azi. Wasu malamai da shugabannin addini sun nuna goyon baya, yayin da wasu ke ganin hakan zai buɗe ƙofa ga siyasa.

Abin da ya rage shi ne yadda gwamnati za ta samu daidaito tsakanin kiyaye ‘yancin addini da kuma samar da doka da zata ke tantance wa’azi da hana wa’azi zama hanyar tayar da tarzoma ko rikita jama’a.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X
Join our WhatsApp Channel
NgHausa

NgHausa

Related Posts

Goodluck Jonathan 2027 – Muhawara kan Halascin Takararsa a Najeriya

Goodluck Jonathan 2027: Muhawara kan kundin tsarin mulkin Najeriya

by NgHausa
October 2, 2025
0

Ana ci gaba da muhawara a Najeriya kan ko tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na da hurumin tsayawa takara a...

Trump Attends the Return of the Remains of the Navy SEAL Who Died in Yemen

by NgHausa
September 6, 2025
0

Dropcap the popularization of the “ideal measure” has led to advice such as “Increase font size for large screens and...

Amaryar TikTok Ta Fadi Matsalar da Jaruman Kannywood ke Fuskanta

Amaryar TikTok Ta Fadi Matsalar da Jaruman Kannywood ke Fuskanta

by NgHausa
May 6, 2025
0

Hafsat Tuge, wadda aka fi sani da Amaryar TikTok, ta ce mutane suna kallon 'yan fim mata da wani kuskuren...

Garba Muhammad: Daga Cikon Benci Zuwa Tauraro a Fim

Garba Muhammad: Daga Cikon Benci Zuwa Tauraro a Fim

by NgHausa
December 24, 2024
0

Fitaccen jarumin nan da ya shahara a duniyar fina-finan Hausa, Garba Muhammad, wanda aka fi sani da Baban Ma'u a...

Recent Posts

  • Kotun Tarayya Ta Ci Gaba da Shari’ar Nnamdi Kanu Ba Tare da Shi Ba Bayan Zargin Rashin Ladabi
  • ASUU Benin Ta Karyata Sabon Ƙarin Albashi: “Ba Zai Hana Ƙaurawar Malamai Ba
  • NELFUND Za Ta Fadada Lamunin Dalibai Zuwa Sana’o’i da Fasaha a Najeriya
  • Willie Obiano Yana Raye Cikin Koshin Lafiya a Amurka – An Karyata Jita-Jitar Mutuwarsa
  • Najeriya 4–1 Gabon: Super Eagles Sun Tsallake Zuwa Wasan Karshe

Recent Comments

  1. Yusuf tanko on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  2. Abdulazeez jibrin on Yadda Zaka Samu Tallafin Kudi a Najeriya (2025): Matakai da Sharuɗɗa
  3. Bashir Gamzaki on COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 PROF. Isah Ali Ibrahim Pantami
  4. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”
  5. IBB on Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”

Archives

  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024

Categories

  • Blog
  • Entertainment
  • Hausa Series
  • KannyWood
  • Labaran Duniya
  • Lafiya
  • Nigeria
  • Nishadi
  • Opportunity
  • Siyasa
  • Sports
  • TAFSEER
  • Wasanni
NgHausa News

© NG Hausa News – 2025

Navigate Site

  • About Us
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Labaran Duniya
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Nishadi
  • KannyWood

© NG Hausa News – 2025

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks