• Latest
  • Trending
  • All
  • News
  • Politics
Hoton tsohon masarautar Kano a lokacin yaƙin basasa na 1893-1895.

Tarihin Yakin Basasa na Kano: Rikicin Sarauta, Sarki Alu da Shigowar Turawa (1893-1903)

September 14, 2025
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

January 9, 2026
AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in  Quarter-Final

AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in Quarter-Final

January 9, 2026
Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

January 9, 2026
Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

January 8, 2026
AFCON 2025: NSC Confirms Super Eagles Players’ Allowances, Bonuses Cleared

AFCON 2025: NSC Confirms Super Eagles Players’ Allowances, Bonuses Cleared

January 8, 2026
Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

January 7, 2026
Nigerian Army Opens DSSC 29/2026 Recruitment for Engineers, Doctors, Others

Nigerian Army Opens DSSC 29/2026 Recruitment for Engineers, Doctors, Others

January 7, 2026
New Tax Regime: CITN Debunks Claims of Tax on Bank Balances

New Tax Regime: CITN Debunks Claims of Tax on Bank Balances

January 7, 2026
Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

January 7, 2026
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
Thursday, January 15, 2026
  • Login
NgNews
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgNews
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Blog

Tarihin Yakin Basasa na Kano: Rikicin Sarauta, Sarki Alu da Shigowar Turawa (1893-1903)

by NgHausa
September 14, 2025
in Blog
0
Hoton tsohon masarautar Kano a lokacin yaƙin basasa na 1893-1895.
491
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Yakin Basasa na Kano: Tarihi da Tasirin sa a Shekaru 131 da suka gabata

Shekaru 131 kenan tun bayan da al’ummar Kano suka tsinci kansu cikin Yakin basasa sakamakon rikicin sarauta tsakanin gidan Sarkin Kano Abdullahi Maje Karofi da gidan Sarkin Kano Muhammadu Bello. Dukkaninsu jikokin Sarkin Kano Ibrahim Dabo ne.

Masana tarihi sun bayyana cewa wannan yaƙin shi ne rikici mafi muni da birnin Kano ya taɓa fuskanta. Wani bature da ya shaida lokacin yaƙin ya kwatanta birnin da cewa “Kanon na ƙarnin jinin mutane” saboda yawan jinin da aka zubar, a cewar Dr. Raliya Zubairu Mahmud, masaniyar tarihi a Kumbotso College, Kano.

Ɗaya daga cikin manyan sakamakon yaƙin shi ne fitowar sabon sarki, wato Sarki Alu a shekarar 1895. Sai dai ba da jimawa ba, Turawan mulkin mallaka suka karɓe iko daga hannunsa a 1903.

Asalin Rikicin Sarauta

Bayan rasuwar Sarkin Kano Ibrahim Dabo, ɗansa Usman ya gaje shi. Daga bisani, ɗan’uwansa Abdullahi Maje Karofi ya hau mulki, sannan bayan rasuwarsa ɗan’uwansu Bello ya zama sarki. Wannan ya sa ƴaƴan Ibrahim Dabo guda uku suka yi sarauta a jere.

Lokacin da Sarkin Kano Bello ya rasu a watan Disamba 1893, Wazirin Sokoto Mu’azu ya kasance a Kano. Shi ne ya sanar da Sultan Abdurrahman labarin rasuwar Bello.

See also  Da ni da Rarara mun dace domin akwai fahimtar juna da aminci a tsakaninmu - Aisha Humaira

A al’ada, bayan rasuwar sarki, ana turawa Sultan sunayen mutane uku domin a zaɓi wanda zai hau mulki. Amma wannan karo Sultan bai bi wannan tsari ba, sai kawai ya naɗa Tukur, ɗan gidan Sarkin Bello, mai shekaru 26 zuwa 28, saboda tsohon alƙawari da ya yi masa.

Sai dai Wazirin ya shaida wa Sultan cewa al’ummar Kano Yusuf suke so. Yusuf shi ne ɗan gidan Maje Karofi, kuma ya rike mukaman Galadima da Ciroma. Wannan ya haddasa babban rarrabuwar kawuna tsakanin Tukurawa da Yusufawa.

Hijirar Yusufawa zuwa Takai

Magoya bayan Yusuf daga gidan Maje Karofi suka yi hijira zuwa Takai, inda suka kafa sansani. A nan ne suka naɗa Yusuf a matsayin sarki, tare da neman mubaya’a daga garuruwan da ke kewaye da Kano.

A watan Agusta 1894, Yusuf da magoya bayansa suka nufi Kano. Amma kafin ya isa, ciwo ya kashe shi a garin Garko, duk da jita-jitar cewa wasu daga cikin danginsa ne suka yi masa kisan gilla domin su ɗora wani daban.

Kafin mutuwarsa, Yusuf ya ambaci ɗan’uwansa Alu (Aliyu Babba) wanda ya kasance ɗan Sultan Abdurrahman ta wurin uwa. Wannan ya sa aka naɗa shi sarki, domin a samu sauƙin karɓuwa daga masarautar Sokoto.

See also  New York: Wani Ya Hallaka Mutane Hudu Ciki Har da Ɗan Sanda A Amurka

Tashin Sarki Alu da Saukar Tukur

Bayan rasuwar Yusuf, aka naɗa Alu a matsayin Sarkin Kano. A ranar 18 Satumba 1894, Alu ya jagoranci magoya bayansa suka shiga Kano. Da jin labarin hakan, Sarki Tukur ya gudu zuwa Katsina.

Sultan Abdurrahman ya nemi taimakon sarakunan Zazzau, Katsina da Kazaure domin a dawo da Tukur, amma duk sun ƙi amincewa.

A watan Maris 1895, aka gwabza yaƙi a Tafashiya tsakanin tawagar Tukurawa da Yusufawa. An illata Tukur bayan dokinsa ya fāɗi, daga baya kuma ya mutu a ranar 16 ga watan Maris 1895. Wannan ne ya kawo ƙarshen Yakin basasa na Kano.

Abubuwan da Yaƙin Basasar Kano ya Haddasa

  1. Mutane da dama sun mutu, har aka ce Kano ta zama “birnin jini.”
  2. Masarautar Sokoto ta ware Sarki Alu duk da zumuncin da ke tsakaninsu.
  3. Iyalai da dama sun yi hijira domin tsira da rayukansu.
  4. Wasu sun bace har abada, ba a sake samun labarinsu ba.
  5. Dangantakar jinin sarauta ta samu mummunar tangarda.
  6. Wasu daga cikin ƴaƴan sarauta sun guji hawa bisa jan kunne.
  7. Tattalin arzikin Kano ya durƙushe saboda kasuwanci ya tsaya cak.
  8. Yakin Basasa ya nuna raunin daular Usmaniyya, abin da ya sauƙaƙa shigar Turawan mulki mallaka.
See also  Kalaman Soyayya Zafafa – Kalmomin Da Ke Taɓa Zuciya da Kauna

Wanene Sarkin Kano Alu?

Alu, wanda ake kira Aliyu Babba ko Alu Maisango, shi ne Sarkin Kano daga 1895 zuwa 1903.

Nasabarsa ta bangaren uba ta fito daga gidan Maje Karofi ɗan Ibrahim Dabo, yayin da ta bangaren uwa kuma ta fito daga Sultan Abdurrahman ɗan Shehu Usman Ɗanfodio. Wannan ya sanya shi ɗan jinin Fulani daga bangarori biyu.

Sarki Alu ya kasance malami kuma jarumi, yana riƙe da makamin gargajiya mai suna Sango, wanda ya sa ake kiran shi “Maisango.”

Ya yi sarauta na tsawon shekaru takwas kafin Turawa su shigo Kano. Bayan suƙa mamaye birnin, Alu ya gudu zuwa gabas amma suka kama shi, suka kai shi Adamawa sannan Lokoja, inda ya zauna har zuwa rasuwarsa a 1926.

Abbas ya hau sarauta ƙarƙashin Turawa

Bayan kama Alu, Wamban Kano Abbas ya ba da shawara a mika wuya ga Turawa. A sakamakon haka, a watan Fabrairu 1903, Turawan mulkin mallaka suka naɗa Abbas a matsayin Sarkin Kano.

Wannan ya nuna karshen ikon gargajiya na masarautar Kano da kuma kafuwar sabon tsarin Turawan mulkin mallaka.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X
Share196Tweet123Share49
NgHausa

NgHausa

  • Trending
  • Comments
  • Latest
Nigerian Army Opens DSSC 29/2026 Recruitment for Engineers, Doctors, Others

Nigerian Army Opens DSSC 29/2026 Recruitment for Engineers, Doctors, Others

January 7, 2026
Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

January 7, 2026
Mohammed Badaru Denies Defection Rumours, Reaffirms Loyalty to APC Amid Jigawa Tensions

Mohammed Badaru Denies Defection Rumours, Reaffirms Loyalty to APC Amid Jigawa Tensions

January 6, 2026
Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”

Brief history of Fatima Hussaini Abbas “Maryam Labarina”

6
COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 SHEIKH MALAM AHMAD TIJJANI YUSUF GURUNTUM

COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 SHEIKH MALAM AHMAD TIJJANI YUSUF GURUNTUM

2
COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 PROF. Isah Ali Ibrahim Pantami

COMPLETE RAMADAN TAFSEER 1446/2025 PROF. Isah Ali Ibrahim Pantami

1
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
NgNews

Copyright © 2017 JNews.

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

Copyright © 2017 JNews.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks