Tinubu: Ba Zan Taba Mayar da Nijeriya Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatin sa ba za ta taba kokarin mayar da Nijeriya kasa mai jam’iyya daya ba. Ya ce yana da cikakken buri na kare tsarin dimokuradiyya da ‘yancin jam’iyyu a cikin kasa.
Tinubu ya bayyana haka ne yayin da yake jawabi a taron hadin guiwa da Majalisar Dokoki na bikin cika shekaru 26 da dawowar demokradiyya a Najeriya.
“Ga wadanda suka yi korafi cewa jam’iyyar APC na kokarin kafa jam’iyya daya, ina tabbatar muku — hakan ba zai faru ba a karkashin shugabancina,” in ji shugaban kasa.
Ya Tuna Irin Gwagwarmayarsa a Siyasa
Shugaba Tinubu ya kuma tuna lokacin da ya kasance gwamna karkashin jam’iyyar adawa a farkon shekarun 2000, yana mai cewa ba zai taɓa manta irin yadda aka takura wa adawa a wancan lokacin ba. Ya ce wannan ne yasa yake da kishin ganin kowane dan siyasa ya samu damar bayyana ra’ayinsa cikin ‘yanci da gaskiya.
Godiya Ga Tsohon Shugaban Kasa Buhari
Tinubu ya mika godiya ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa yadda ya fahimci muhimmancin juyin da ya faru a zaben 1993 — zaben da aka fi danganta da nasarar Cif Moshood Abiola da Alhaji Babagana Kingibe, wanda gwamnatin soja ta soke.
Ya bayyana wannan matsayin Buhari a matsayin wani mataki na gyara kuskuren tarihi, tare da tabbatar da cewa dimokuradiyya na cigaba a Najeriya.
KARSHEN SAKO: Shugaban kasa Tinubu ya bayyana tsayawar sa tsayin daka wajen kare dimokuradiyya, ya kuma jaddada cewa Najeriya zata ci gaba da zama kasa mai jam’iyyu da dama, ba mallakin wata jam’iyya daya ba.