• Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
NgHausa
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgHausa
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Siyasa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

NgHausa by NgHausa
February 23, 2026
in Siyasa
0
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026
491
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

A makon da ya gabata ne, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanya hannu kan sabuwar dokar zaɓen ƙasar ta 2026, wadda aka yi wa gyaran fuska. Shugaban ya sa hannu kan dokar – wadda ta ƙunshi ƙa’idojin yin zaɓukan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomin yankin birnin tarayya.

A lokacin sanya hannu kan dokar, Tinubu ya ce: “Babu batun siyasa a cikin wannan gyare-gyare, abu ne na tsari, ƙoƙari ne na cike giɓi da ƙarfafa tsari da kuma samar da tsaftatacciyar hanya ga masu tsarawa da kuma masu yin zaɓuka.”

Shugaban ya sanya hannu kan dokar ne bayan hargitsin da aka samu a zaurukan majalisar tarayyar ƙasar da ma zanga-zangar da ƙungiyoyin fararen hula suka yi game da gyaran da aka yi wa dokar.

‘A Yanzu Babu Dalaget’

Ɗaya daga cikin manyan gyare-gyaren da aka yi wa dokokin zaɓen shi ne hanyoyin da jam’iyyu ke bi wajen zaɓukan fitar da gwani. A baya, jam’iyyun siyasa kan yi amfani da wasu wakilai na musamman da ake kira ‘deliget’, waɗanda ake zaɓa a matakai daban-daban, tun daga matakin akwati da mazaɓa har zuwa matakin ƙasa.

See also  Gwamnatin Kano Ta Shirya Yi Wa Tubabbun Ƴan Daba Afuwa

Farfesa Kamilu Sani Fagge na Jami’ar Bayero da ke Kano ya ce a gyaran fuskar da aka yi wa dokar zaɓen ta 2026, an rusa wannan tsari na dalaget. A ra’ayinsa, tsarin “deliget na daga cikin abubuwan da suka gurɓata tsarin fitar da ƴantakara da ma zaɓen Najeriya baki ɗaya.”

“Saboda su deliget ɗin nan, idan suka je zaɓen fitar da gwani ciniki suke yi, sukan karɓi kuɗin kowane ɗan takara, kuma idan ba su zaɓe shi ba ba za su mayar masa da kuɗinsa ba,” in ji shi.

A yanzu, sabuwar dokar ta tanadi hanyoyi guda biyu na gudanar da zaɓukan fitar da gwani na ƴantakara, wato: masalaha da ƴar tinƙe (ƙato-bayan-ƙato).

Me Ake Nufi da Masalaha?

Masalaha shi ne masu sha’awar tsayawa takarar gujera ɗaya a jam’iyyar ɗaya su zauna tsakaninsu su yi sasanci domin janye wa mutum guda. A wannan zama, ƴantakarar da shugabannin jam’iyyu za su zauna tare da ƙulla alƙawura domin cimma yarjejeniya.

Sabuwar dokar ta yi tanadin cewa idan wannan hanya ba ta kai ga nasara ba, to sai a je hanya ta biyu — wato ƴar tinƙe.

See also  PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

Me Ake Nufi da Ƴar Tinƙe?

Farfesa Fagge ya bayyana cewa a ƴar tinƙe, ƴan jam’iyya masu rajista za su fita domin zaɓen mutumin da suke so ya tsaya wa jam’iyyar takara. Akan gudanar da wannan zaɓe a matakai daban-daban, kama daga mazaɓu zuwa ƙaramar hukuma, jiha, da kuma matakin tarayya.

Hanyoyin biyu na ƴar tinƙe su ne: bi layi a bayan ɗantakarar da ake so a ƙirga yawansu, ko kuma zaɓe a asirce ta amfani da akwati.

A Ina Za a Yi Zaɓukan?

A baya, akan gudanar da zaɓukan fitar da gwanaye a manyan tarukan jam’iyyun. A yanzu ma haka za a yi, amma a matakai daban-daban — daga matakin mazaɓa zuwa ƙaramar hukuma da jiha.

A matakin zaɓen gwamna ko shugaban ƙasa, za a gudanar da zaɓukan a wurare daban-daban a rana guda. “Idan za a yi na gwamnoni saboda yawan ƴan jam’iyyar za a gudanar da zaɓukan ne a kowace ƙaramar hukumar, haka ma na shugaban ƙasa za a yi a kowace jiha,” in ji Farfesa Fagge.

‘Shi Ma Tsarin Na Da Nasa Matsaloli’

Manufar yi wa dokar gyara dai shi ne magance matsalolin da ake yawan samu a zaɓukan fitar da gwanaye — lamarin da a wasu lokutan ke ƙarewa a kotuna, ko ma ya janyo asarar kujerun da jam’iyyar ta riga ta ci a babban zaɓe. Alal misali, a shekarar 2019, jam’iyyar APC ta rasa kujerun gwamna da na majalisar dattawa da ta wakilai a jihar Zamfara bayan matsaloli masu alaƙa da zaɓukan fitar da gwani.

See also  Malam Nasiru El-Rufai: Ba Zan Nemi Takara a 2027 Ba

Duk da haka, Farfesa Fagge ya gargaɗi cewa sabon tsarin ma yana ƙunshe da nasa matsalolin. “A wasu lokutan ƴan takara kan karɓi katunan jam’iyyar daga hannun ƴan jam’iyyar ta hanyar ba su kuɗi, sai kuma ya kira wasu da ma ba ƴan jam’iyyar ba ya ba su kuɗi da waɗannan katuna domin su zaɓe shi.”

Har ila yau, ya ce ƴan takara sukan tayar da fitina a lokacin ƙirge-ƙirge — musamman idan suka hango cewa abokin hamayyarsu na kan gaba — har ta kai ga dakatar da aikin ƙirge-ƙirge da zargin magudi.

Share this:

  • Share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Share on X (Opens in new window) X
Tags: BbchausaLabaran DuniyaLabaran siyasaLeadership Hausa
NgHausa

© 2026 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

Navigate Site

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

© 2026 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

Enable Notifications OK No thanks