Yakubu Muhammad Ya Bayyana: Zai Iya Auren Mace Irin Samira Daga Shirin Garwashi

Yakubu Muhammad, Fitaccen Jarumin Kannywood, ya bayyana cewa zai iya auren mace irin Samira da ke cikin shirin Garwashi. Wannan bayani ya jawo ce-ce-ku-ce tsakanin masu kallo, domin mutane da dama suna ganin halayen Samira a cikin shirin a matsayin wasu da ba su dace da rayuwar aure ba. Sai dai Yakubu Muhammad ya ce a zahiri, yana kallon abubuwa daban da yadda ake kallon su a fim.
Yakubu Muhammad ya kuma yi ƙarin bayani dangane da rawar da yake takawa a cikin fina-finai masu dogon zango da yake fitowa. Wasu daga cikin waɗannan fina-finan sun haɗa da Garwashi, inda yake taka muhimmiyar rawa, da Labarina, wanda ya shahara sosai, da kuma Gidan Sarauta, fim da ke bayani kan rayuwar fada. A cewarsa, kowanne daga cikin waɗannan fina-finan yana da saƙon da yake isarwa ga masu kallo.
A cewar Yakubu Muhammad, shirin Garwashi ya na ɗauke da darussa masu muhimmanci da suka shafi rayuwar yau da kullum. Ya ce yana alfahari da rawar da yake takawa a fina-finan Kannywood, domin yana amfani da su wajen ilmantarwa da nishaɗantar da al’umma. Ya kuma gode wa masoyansa bisa goyon bayan da suke ba shi a duk fina-finan da yake fitowa.