• Latest
  • Trending
  • All
  • News
  • Politics
Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi

Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi

February 2, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Zaɓen Najeriya Ta 2026

February 23, 2026
PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

PDP ta Dora Laifi kan Dokar Zaɓe ta 2026 kan Ƙarancin Masu Kaɗa Kuri’a a Zaɓen FCT

February 22, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Sheikh Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum (Yamma)

February 21, 2026
Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

Complete Ramadan Tafseer 1447/2026 Prof. Isah Ali Ibrahim Pantami

February 19, 2026
AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

AFCON 2025: Vladimir Petkovic Admits Nigeria Deserved 2-0 Quarter-Final Win Over Algeria

January 11, 2026
Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

Businesses Exploit New Tax Laws to Raise Prices Nationwide, Nigerians Lament

January 10, 2026
Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

Brahim Diaz Shines as Morocco Beat Cameroon to Reach AFCON 2025 Semi-Finals

January 9, 2026
Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

January 9, 2026
AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in  Quarter-Final

AFCON 2025:Nigeria vs Algeria Super Eagles Face Desert Foxes in Quarter-Final

January 9, 2026
Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

Arsenal Held to 0-0 Draw by Liverpool as Title Push Stalls at Emirates

January 9, 2026
Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

January 8, 2026
  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us
Monday, March 2, 2026
  • Login
NgHausa
  • Home
    • Home – Layout 1
    • Home – Layout 2
    • Home – Layout 3
    • Home – Layout 4
    • Home – Layout 5
  • News
    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Donald Trump Warns of More US Military Strikes in Nigeria Over Attacks on Christians

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Rivers APC Rejects Impeachment Move Against Governor Fubara, Warns Assembly

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Court Orders Interim Forfeiture of 57 Properties Linked to Ex-AGF Abubakar Malami

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    Fresh Terror Attacks Hit Kwara, Katsina, Kaduna as Journalists, Others Abducted

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    AFCON 2025: Eric Chelle Hails Super Eagles’ 4-0 Win, Warns Against Complacencya

    Trending Tags

    • Donald Trump
    • Future of News
    • Climate Change
    • Market Stories
    • Election Results
    • Flat Earth
No Result
View All Result
NgHausa
No Result
View All Result
  • Siyasa
  • Nishadi
  • Wasanni
  • TAFSEER
Home Blog

Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi

by NgHausa
February 2, 2025
in Blog
0
Nafison fitowa a matsayin masifaffiya a cikin Film inji Fa’iza Abdullahi
492
SHARES
1.4k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Faiza Abdullahi, jarumai dake fitowa a matsayin matar Kofur Audu a shirin Dadin Kowa, ta bayyana haka ne ga mujallar film a lokacin tattaunawar ta da wakilin ta.

Mu fara da jin tarihin rayuwar ki.


FA’IZA: Na farko, suna na Fa’iza Abdullahi. An haife ni ne a cikin Jihar Bauchi, a wani gari da ake kira Jalaf a Ƙaramar Hukumar Damban. A can na yi karatu na girma duk a can. A yanzu dai ban wuce shekara 26 ba, sai kuma a yanzu da na kasance a garin Kano ina gudanar da sana’a ta ta aikin fim.

Shin fim ne ya kawo ki Kano kuma a wane lokacin kika zo?


FA’IZA: To gaskiya, zuwa na Kano zai kai shekara bakwai a yanzu kuma harkar fim ce ta kawo ni Kano, don in ban da ta dalilin fim ban san kowa a Kano ba, ban ma taɓa zuwa ba sai ta sanadin zan yi fim.

Da yake an fi sanin Fa’iza Abdullahi a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’ a matsayin matar Kofur Audu, ko kin taɓa yin wani fim ɗin kafin ki fara ‘Daɗin Kowa’?

See also  Hadizan Saima Ta Ba da Aminci Kan Abubuwan Da Ke Saka Ta Farin Ciki


FA’IZA: Gaskiya ban taɓa yin wani fim ba sai ‘Daɗin Kowa’, don da shi na fara. Ba zan manta ba lokacin da na zo garin Kano haka, ina zuwa Zoo Road akwai wani da na sani wanda shi ne darakta a fim ɗin a lokacin, nakan je na gaishe su, duk da ban ma san shi waye ba a lokacin, sai wata rana ya kira ni ya ce na zo ana nema na zan yi sin ɗaya a wani aiki, to ban ma san yadda abin yake ba sai da na je. To da haka na fara, har aka zo daga baya ake kira na lokaci zuwa lokaci. Kuma lokacin da na fara fitowa a cikin ‘Daɗin Kowa’, a matsayin ‘yar tuwo-tuwo ce mai sayar da abinci, kuma ba mu da gida, ni kaɗai ce a wajen abinci sai masu zuwa su saya.

See also  Dangote Ya Rage Farashin Litar Mai Zuwa ₦820

Shin akwai bambanci tsakanin rayuwar Fa’iza Abdullahi ta zahiri da kuma ta shirin ‘Daɗin Kowa’?


FA’IZA: To akwai bambanci sosai, saboda ka ga dai ita Fa’iza Abdullahi a zahiri ba ta faɗa, sannan tana girmama na gaba da ita da sauran abubuwa na girmamawa. Amma ita Bilkisu a cikin shirin ‘Daɗin Kowa’ ba ta da kunya, ba mu’amala mai kyau, ko gidan su ma ba ta girmama su ba. Haka gidan mijin ta ma ba ta raga wa kowa ba. To amma sai ya kasance mutane a gari suna kallo na a matsayin Bilkisu maimakon su kalle ni a matsayin Fa’iza Abdullahi. Da yawa abin da na fi fuskanta a rol ɗin da nake, sai mutane idan mun haɗu su rinƙa cewa Allah ya ƙara. Abin da nake yi wa Kofur Audu suna jin daɗi saboda macuci ne azzalumi. Wasu kuma suna cewa bai kamata ba, na rinƙa sassauta masa.

See also  EFCC ta kama Murja Kunya saboda zarginta da 'wulaƙanta takardun naira'

Wane rol kika fi so a saka ki?


FA’IZA: Gaskiya duk da a cikin fim babu rol ɗin da ba na takawa, na fi so a saka ni na fito a masifaffiyar mace. Ina son na fito na yi masifa yadda rai na yake so. Don ka ga ko rol ɗin da nake yi a yanzu a cikin fim ɗin ‘Muhalli’ wani rol ne da na fito a matsayin matar aure amma marar mutunci, masifaffiya. Don haka ina son rol ɗin sosai na fito a matar aure marar mutunci, marar tarbiyya. Don haka nake son rol ɗin, don an ba ni dama ina yin masifa yadda rai na yake so, kuma ga ni matar mai kuɗi, ina jin daɗin rayuwa, ga kuma ina zuba masifa. Don haka ina jin daɗi sosai da wannan rol ɗin.

Share this:

  • Share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Share on X (Opens in new window) X
Share197Tweet123Share49
NgHausa

NgHausa

NgHausa

Copyright © 2017 JNews.

  • Privacy Policy
  • Terms and Conditions
  • Disclaimer
  • About Us
  • Contact Us

Follow Us

No Result
View All Result
  • Home
  • News
    • Politics

Copyright © 2017 JNews.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
Enable Notifications OK No thanks